News
Al’ummar Mazabar Gobirawa Na Cikin Matsanantiyar Damuwa Akan Tsayawar Aikin Fadada Asibitocin 3
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Al’ummar Mazabar Gobirawa na cikin matsanantiyar damuwa tare da bayyana korafin su kan yadda aikin fadada Asibitoci guda 3 ya tsaya cik wanda wakilin Dala a majalisar Dokokin jihar Kano Hon. Lawan Hussain ke gudanarwa a mazabar su ta Gobirawa tun bayan kammala aikin da kimanin kaso 65 wanda ake zargin masu yin aikin da Jan kafa.
Korafin na zuwa ne tabakin daya daga cikin jagororin yankin Comrade Murtala wanda shine Diraktan dake lura da Kafar sada zumunta ta zamani a karkashin KUNGIYAR FITILAR AL’UMMAR GOBIRAWA a zantawar da yayi da manema labarai kan aiyukan da Kungiyar tasa a gaba zuwa karshen shekarar 2024.
Kungiyoyin Da Ke Doka Gasar Premier Za Su Kaɗa Ƙuri’a Kan Bukatar Soke Na’urar VAR
Comrade Murtala ya zargi wanda suke gudanar da aikin fadada Asibitoci da daina zuwa gurin aikin baki daya tare da kwashe kayan su a wasu daga cikin asibitocin.
Murtala ya bayyana asibitocin guda 3 da ayyukan su ya tsaya kamar haka:
Asibitin Gidan Dagacin Gobirawa, Asibitin Tudun bojuwa sai Asibitin Umma Zariya dake Unguwar Filin Durimi inda ya bayyana tasiri da gudun mawar da aikin zai kawo ta fuskar lafiya idan an kammala a yankin.
A karshe ya godewa Dan majalisar a madadin Al’ummar mazabar Gobirawa dangane da kokarin da yayi na kawo irin Wannan aiki har gudu uku a cikin kankanin lokaci tun bayan komawarsa majalisa a karo na biyu.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
