News
Yanzu-yanzu: Gwamnati Ta Ayyana Litinin A Matsayin Ranar Hutu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya ayyana ranar 8 ga watan Yuli a matsayin ranar hutu domin murnar shiga sabuwar kalandar Musulunci, a watan muharram 1446AH.
Alhaji Auwal Manu-Dogondaji, kwamishinan Harkoki Gwamatin jihar ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Birnin Kebbi ranar Juma’a.
Hukumar Sufurin Jiragen Sama NCAA Ta Dakatar Da Jerin Jiragen Alfarma 10 Daga Yin Shawagi A Najeriya
A cewarsa, ranar 1 ga watan Muharram ita ce 7 ga watan Yuli, don haka saboda muhimmancin da gwamnati ke da ita ga sabuwar shekara ta Musulunci, ta yanke shawarar mayar da ranar hutu daga 7 ga watan Yuli zuwa 8 ga watan Yuli.
Manu-Dogondaji ya taya al’ummar musulmi murnar shigowar sabuwar kalandar Musulunci, inda ya bukaci al’ummar musulmi da su ci gaba da gudanar da addu’o’in zaman lafiya, tsaro da ci gaban jihar Kebbi da kasa baki
“Ina mika sakon taya murna ga gwamnan ga daukacin al’ummar musulmi a fadin duniya,” in ji kwamishinan.
