News
Majalisar Dattawa ta tsige Sanata Ndume daga kujerarsa ta mai tsawatarwanta.
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Majalisar Dattawa ta tsige Sanata Ndume daga kujerarsa ta mai tsawatarwanta.
Sauke Ali Ndume daga kujerar na da nasaba da zargin Gwamnatin Shugaba Tinubu da rashin daukar mataki wajen magace yunwa da ke addabar al’ummar Najeriya.
Gobara Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Iyalan Kwamishinan Ilimi Mai Zurfi Na Kano
Ndume wanda shi ma dan Jam’iar APC mai mulki ne ya kuma yi zargin cewa Shugaba Kasa Bola Tinubu bai san halin da al’umma ke ciki ba, kuma akwai wadanda suke hana shi ganin jama’a da yin magana a kan al’amara.
A zaman ranar Larba shugaban majalisar, Godswill Akpabio, ya gabatar da kudurin tsige Ndume, wanda kuma yan Jam’iyyar APC suka goyi baya.
A halin da ake ciki majalisar ta maye gurbin Ndume da Sanata Tahir Mungono (Borno ta Arewa) a matsain sabon mai tsawatarwa.
Wata wasikda da uwar Jam’iyyar APC ta aike wa mambobinta a majalisar ta bukaci Sanata Ndume ya fice daga cikinta ya koma duk jam’iyyar adawa da yake sha’awa.
Wasikar na dauke da sa hannun Shugaban APC na Kasa Abdullahi Ganduje, da Sakatare, Barista Ajibola Bashiru.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
