News
Zasu Gurfanar Da Wasu Daga Cikin Yan Kasuwar Singa A Kotu Akan Zargin Karin Fashin Kayayyakin Masarufi —Muhyi Magaji
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban hukumar karbar korafe korafe da Hana cin hanci da rashawa ta Jihar Kano Muhyi Magaji Rimin Gado ya ce zasu gurfanar da wasu daga cikin yan kasuwar Singa a kotu kan zargin yiwa mutane Karin fashin kayayyakin masarufi bayan kammala zanga-zangar lumana.
Muhyi ya bayyana hakane ta cikin shirin barka da hantsi na gidan radiyon Freedom ya ce hukumar zata gurfanar da wasu daga cikin yan kasuwar Singa ne sakamakon zargin su da yiwa mutane Karin farashin kaya ba bisa doka.
Sanatan Kano Ya Bayyana Yadda Sanatoci Suke Samun Naira Miliyan 21 A Duk Wata
Haka zalika hannu guda kuma ya ce anna gudanar da bincike kan zargin karkatar da akalar shinkafar tallafi da gwamnatin tarayya ta baiwa Al’ummar Jihar Kano.
Ya kuma ce yanzu haka tuni hukumar ta samo oda daga kotu don fara daukar mataki na farko gabanin zuwa gaban alkalin Kai tsaye.
Muhyi Ya kuma kara da cewa hukumar za taci gaba da sanya Ido don ganin an tabbatar da aiwatar da dai-daiton da aka Samar kan Karin farashin kayayyakin masarufin.
Muhyi Magaji rimin gadon ya bayyana hakane ta cikin shirin barka da hantsi Wanda kuma daga bisani abokin Aiki Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya zanta dashi kan batun, inda yace, hukumar tasa zata gurfanar da wasu daga cikin yan kasuwar singar ne sakamakon zarginsu da yiwa mutane Karin farashin kaya bayan kammala zanga-zangar lumana.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
