Connect with us

News

Zasu Gurfanar Da Wasu Daga Cikin Yan Kasuwar Singa A Kotu Akan  Zargin Karin Fashin Kayayyakin Masarufi  —Muhyi Magaji

Published

on

Ƴan Siyasa Na Haɗa Kai Da Ma’aikata Wajen Wawure Dukiyar Al’umma – Muhyi Magaji
Shugaban hukumar karbar korafe korafe da Hana cin hanci da rashawa ta Jihar Kano Muhyi Magaji Rimin Gado

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

Shugaban hukumar karbar korafe korafe da Hana cin hanci da rashawa ta Jihar Kano Muhyi Magaji Rimin Gado ya ce zasu gurfanar da wasu daga cikin yan kasuwar Singa a kotu kan zargin yiwa mutane Karin fashin kayayyakin masarufi bayan kammala zanga-zangar lumana.

Advertisement

Muhyi ya bayyana hakane ta cikin shirin barka da hantsi na gidan radiyon Freedom ya ce hukumar zata gurfanar da wasu daga cikin yan kasuwar Singa ne sakamakon zargin su da yiwa mutane Karin farashin kaya ba bisa doka.

Sanatan Kano Ya Bayyana Yadda Sanatoci Suke Samun Naira Miliyan 21 A Duk Wata

Haka zalika hannu guda kuma ya ce anna gudanar da bincike kan zargin karkatar da akalar shinkafar tallafi da gwamnatin tarayya ta baiwa Al’ummar Jihar Kano.

Advertisement

Ya kuma ce yanzu haka tuni hukumar ta samo oda daga kotu don fara daukar mataki na farko gabanin zuwa gaban alkalin Kai tsaye.

Muhyi Ya kuma kara da cewa hukumar za taci gaba da sanya Ido don ganin an tabbatar da aiwatar da dai-daiton da aka Samar kan Karin farashin kayayyakin masarufin.

Advertisement

Muhyi Magaji rimin gadon ya bayyana hakane ta cikin shirin barka da hantsi Wanda kuma daga bisani abokin Aiki Ibrahim Abdullahi Soron Dinki ya zanta dashi kan batun, inda yace, hukumar tasa zata gurfanar da wasu daga cikin yan kasuwar singar ne sakamakon zarginsu da yiwa mutane Karin farashin kaya bayan kammala zanga-zangar lumana.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending