Business
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
SAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnati Za Ta Fara Sayar Wa Ɗangote Ɗanyen Mai Da Naira A Watan Oktoba
Ministan kudi kuma mai kula da tattalin arzikin Nijeriya Wale Edun, ya ce gwamnatin tarayya za ta fara sayar da danyen mai ga Dangote da sauran matatun man kasar nan a farashin Naira daga ranar 1 ga Oktoba, 2024.
Ana Tsare Da Masu Zanga-Zangar Tsadar Rayuwa Fiye Da 1000 A Najeriya
Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Litinin a taro na biyu na taron kwamitin aiwatarwa kan batun sauya farashin sayar da danyen mai zuwa Naira da shugaba Bola Tinubu ya kafa.
Sanarwar ta ce, an kuma samar da sabbin bayanai kan matatun mai na Fatakwal da Dangote, inda ake sa ran za a samu karin yawan man da ake samarwa daga watan Nuwamba na shekarar 2024. Sai dai, sanarwar ba ta bayyana lokacin da matatar man Fatakwal za ta fara aiki ba.
Kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL) ya dage ranar fara aikin matatar mai ta Fatakwal a karo na shida tun bayan da Mele Kyari ya zama shugaban kamfanin.
-
News2 days ago
Wani Matashi Mai Shekaru 18 Ya Rasa Ransa Bayan Fadawa Cikin Ruwa A Kano
-
News1 day ago
Kaduna, Nasarawa, Zamfara Da Wasu Jihohi 10 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa —NiMet
-
News2 days ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
