Connect with us

News

‘Yan Sanda 32 Ne Kawai Ke Tsare Kauyuka 200 A Katsina – Gwamnatin Katsina

Published

on

images (4)

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

Gwamnan jihar Katsina Dikko Ummar Radda ya sake yin tsokaci kan kalubalen tsaro da ke ci gaba da addabar jihar.

Advertisement

Yayin da yake hira da DW Hausa, gwamnan ya ce jami’an ‘yan sanda 32 ne kawai ke sintiri a karamar hukuma daya a jihar.

Asibitin Best Choice Ya Kaddamar Da Sabuwar Na’urar Jarirai Ta (Jaundice) Irinta Ta Farko A Arewacin Najeriya

Gwamnan, wanda bai bayyana ko wane daga cikin kananan hukumomin ba, ya ce ya kunshi unguwanni 10 da kauyuka sama da 200.

Advertisement

A cewarsa, a cikin jami’an 32, bindigu guda tara ne kawai ke da su, inda guda biyar kacal suke aiki.

Ya ce a yanzu haka a Katsina akwai karamar hukuma mai ‘yan sanda 39 da bindigu guda tara, kuma bindigogin da zasu iya aiki su biyar ne.

Advertisement

Mun bullo da wani shiri wanda duk wata al’umma da ke shirye ta kare kanta, za mu ba su goyon baya da horon da ya dace don kare kai kafin zuwan jami’an tsaro.

Katsina ta sha fama da munanan hare-hare daga ‘yan bindiga.

Advertisement

Ko a kwanakin baya Gwamna Radda ya yi kira ga al’ummar jihar da su dauki matakan kare kansu daga hare-haren ‘yan bindiga.

Ya yi wannan jawabi ne a wani taro da aka yi a Daura.

Advertisement

A cikin wani faifan bidiyo da ya yadu, Radda ya fusata sosai, ya kuma bukaci malaman addinin Musulunci da su fadakar da ‘yan kasar muhimmancin kare kai kamar yadda addinin Musulunci ya tanada.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending