Connect with us

News

Sanatocin Arewacin Najeriya 12 Da Suka Gaza Gabatar Da Ƙudiri A Watanni 15 — Rahoto

Published

on

Sanatocin Arewa 12 Da Suka Gaza Gabatar Da Ƙudiri A Watanni 15

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD TUKUNTAWA

Wani bincike da Jaridar WIKKITIMES ta yi ya bayyana cewa sanatoci 12 daga  jihohin arewacin Nijeriya ba su gabatar da kowanne ƙudiri ba a cikin watanni 15 na farkon wa’adin majalisar dokoki ta 10, wadda ta fara aiki tun ranar 13 ga Yuni, 2023.

Advertisement

Waɗannan sanatoci na wakiltar yankuna da ke fama da matsaloli masu tsanani irin su rashin tsaro, talauci, rashin ingantaccen ababen more rayuwa, da rashin aikin yi.

Shugaba Tinubu Ya Aika Wa Majalisun Dokoki Dokar Sake Fasalin Haraji A Najeriya

Daga cikin Sanatocin da ba su gabatar da ƙudiri ba akwai Abdul Ningi (Bauchi ta tsakiya), Musa Mustapha (Yobe ta Gabas), da Ahmed Lawan (Yobe ta Arewa), wanda shi ne tsohon Shugaban Majalisar Dattawa.

Advertisement

Wasu sanatocin kuma sun fito daga jihohin Adamawa, Taraba, Sokoto, da Filato, waɗanda duk suna fama da manyan matsalolin tattalin arziki da zamantakewa.

Duk da matsalolin da ke addabar waɗannan yankuna — kamar rashin ingantaccen kiwon lafiya, ilimi, da ababen cigaban rayuwa — wadannan sanatoci ba su ɗauki matakin samar da doka ba don magance wadannan matsaloli masu tsanani.

Advertisement

LEADERSHIP HAUSA ta ruwaito cewa masana sun yi Allah wadai da rashin wannan aiki na ƴan majalisar, suna kallon hakan a matsayin gazawar wakiltar muradun al’ummominsu da kuma ɗumama kujera.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending