News
Rundunar Yan Sanda Ta Kori Jami’an Ta 3 Saboda Kisan Dalibin Kwaleji
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Rundunar yan sandan jihar Kwara ta sanar da korar jami’an ta 3 bisa zargin su da taka rawa a kisan wani dalibin kwalejin kimiyya da fasaha ta jihar a babban birnin jihar Ilorin mai suna Qoyum Abdulyekeen Ishola.
Lamarin kisan daya faru ranar 4 ga watan Satumba ya samu kalubalanta da yin ala wadai, wanda hakan yasa aka mayar da binciken kisan zuwa babban birnin tarayya Abuja, karkashin jagorancin shugaban yan sandan kasa Kayode Egbetokun.
Ɗalibi ɗan shekara 15 ya maka ma’aikatar ilimi, da JAMB da NUC a gaban kotu
Jami’an da aka kora sun hadar da Abiodun Kayode, Samuel da Oni Philip.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar DSP Toun Ejire-Adeyemi, tace an samu jami’an da laifukan da suka shafi cin hanci da Kuma yin amfani da karfi a inda bai kamata ba.
Tace nan gaba kadan za’a gurfanar da jami’an da aka kora.
Daily Trust ta ruwaito cewa an kashe dalibin lokacin zanga zangar karin farashin man fetur
