Connect with us

News

A Gobe Laraba Shugaba Tinubu Zai Yi Tafiya Zuwa  Faransa kwanaki Hudu 4  Da Dawowarsa Daga Kasar Barazil 

Published

on

FB IMG 1732637934976

 

A gobe  Laraba ne shugaban kasa Bola Tinubu zai bar Abuja domin fara ziyarar aiki ta kwanaki uku a kasar Faransa bayan amsa gayyatar da  Emmanuel Macron shugaban kasar Faransa  ya yi .

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Ziyarar wadda za ta mayar da hankali kan karfafa dangantakar siyasa da tattalin arziki, da al’adu da samar da karin damammaki na hadin gwiwa, musamman a fannin noma, tsaro, ilimi, kiwon lafiya, harkar makamashi, ci gaban matasa da ayyukan yi da kirkire-kirkire.

Advertisement

 

A taron ana   kyautata zaton cewa, za’a samar da gagarumar nasara ga Nijeriya kamar Yadda Jaridar Daily Trust ta rawaito.

Advertisement

 

A cewar sanarwar da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu da mai dakinsa, Sanata Oluremi Tinubu, za su isa kasar a ranar Alhamis a gidan tarihi na sojojin Faransa, ‘Les Invalides da Palais de l’Élysée,’ mai shekaru 350 wanda Macron da matarsa, Brigitte za su tarbe su, wanda daga bisani za su shiga cikin tattaunawar.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, shugaba Tinubu zai sami rakiyar manyan ma’aikatan gwamnatin a  wannan tafiya.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending