News
Gwamnan Kano Ya Zargi Jam’iyyun Adawa Da Rura Wutar Rikicin Siyasa A Kano
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya zargi ’yan siyasa a jam’iyyun adawa da rura wutar rikicin al’umma da tabarbarewar siyasa a Kano.
Gwamna Yusuf ya yi nuni da ga yatsa a lokacin da yake yiwa manema labarai karin haske a taron majalisar zartarwa ta jihar a ranar Laraba, ya sha alwashin daukar tsauraran matakan da suka dace domin dakile sake barkewar ‘yan daba.
Fannoni Da Ke Kan Gaba A Kasafin Kudin 2025 Da Shugaba Tinubu Ya Gabatar
Martanin Gwamnan ya biyo bayan rikicin baya-bayan nan da ya barke tsakanin wasu da ake zargin ‘yan bangar siyasa ne da suka yi ta’addanci a kan wata kungiyar ‘yan siyasa.
Advertisements
