News
Jami’an Hukumar NAFDAC Sun Ankarar Da Jama’a A Kan Wani Jabun Maganin Zazzabin Cizon Sauro
DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA
Hukumar kula da sahihanci da ingancin magunguna da abinci a kasa (NAFDAC) ta ankarar da jama’a a kan wani jabun maganin zazzabin cizon sauro mai suna ”Paludex” wanda ake siyar da kwayoyin sa da na ruwa a shagunan magani a fadin Naeriya
WIKKI TIMES ta ruwaito cewa a wani jawabi da ta fitar a shafin ta na dandalin zumunta ‘X’, NAFDAC ta bayyana cewa maganin, ‘Paludex’, wanda aka nuna ya kunshi sinadaran ‘Artemether/Lumefantrine, wani kamfani ne mai suna ‘Impact Pharmaceutical Ltd, wanda ya ke fili mai lamba 33A/33AB a rukunin masana’antu na Emene a jihar Enugu, ya ke samar da shi.
Gwamnan Kano Ya Zargi Jam’iyyun Adawa Da Rura Wutar Rikicin Siyasa A Kano
Kazalika, jawabin ya bayyana sunan MD Life Sciences Ltd da ke rukunin masana’antu na Emene a jihar Enugu, a matsayin kamfanin da ke kasuwancin maganin.
NAFDAC ta bayyana cewa bayan samfurin maganin na kwaya, akwai wani samfurin Paludex (180mg/1080mg) na ruwa domin amfanin kananan yara.
Hukumar NAFDAC ta ce sakamakon binciken inganci da aka gudanar a dakin gwaje-gwaje na hukumar lafiya ta duniya (WHO) da ke kasar Germany ya nuna cewa babu sinadaran (API) da za su yaki kwayoyin cutar zazzabin cizon sauro a cikin magungunan.
A cewar jawabin, dukkan magungunan babu su a cikin jerin kayan da hukumar NAFDAC ta taba yi wa rijista tare da bayyana cewa hatta lambar NAFDAC da aka rubuta a magungunan ta karya ce.
NAFDAC ta ce ta sanar da dukkan shugabannin ofisohin ta da ke fadin Nigeria a kan su gudanar da bincike a jihohin su tare da kwacewa da kuma dakile yada maganin duk inda aka gano shi.
Har ila yau, NAFDAC ta yi kira ga manyan ‘yan kasuwar magunguna, ma su aiki a cibiyoyin lafiya, da ma marasa lafiya a kan su lura sosai domin tabbatar da cewa ba a cigaba da amfani da maganin ba.
NAFDAC ta yi kira ga jama’a a kan su guji siyan magunguna a wurare ko shagunan da basu da sahalewa ko lasisi daga hukuma.
A karshe, NAFDAC ta bukaci jama’a su sanar da ita duk wani magani da ba su yarda da shi ba zuwa ofishin hukumar mafi kusa ko kuma ta hanyar kiran lambar su a kan 0800-162-3322 ko kuma ta hanyar sako a adireshin su na email: sf.alert@nafdac.gov.ng.
