Connect with us

News

Duk Masu ƙin Biyan Haraji Za Su Danɗana Kuɗarsu A Shekarar  2025 – Gwamnnan  Kano 

Published

on

Advertisements
ads

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

 

 

 

 

Advertisement

Gwamnatin Kano ta sha alwashin hukunta duk masu ƙin biyan haraji daga shekarar 2025 a matsayin wani ɓangare na kawo gyara ga ɓangaren haraji a jihar.

 

Sanarwar hakan  na ƙunshe ne cikin wani jawabi da Sanusi Bature Tofa yayi , mai magana da yawun gwamnan Kano, Abba Yusuf, a makon jiya.

 

A cikin jawabin da  shugaban hukumar tattara haraji (KIRS) ta Jihar Kano yayi Dr Zaid  ,yace gwamnatin tayi wannan  gargaɗi ne domin  yunƙurin bunkasar  gwamnati na inganta harkokin haraji a jihar.

 

Advertisement

Abubakar ya ce za a kawo gyaran ne domin inganta harkokin haraji da inganta karɓar haraji da tabbatar da makamantansu.

 

Ya ce gwamnatin Kano na sa ran tattara haraji da ya kai sama da Naira biliyan 20 a kowanne rubu’i na shekarar 2025.

 

Shugaban ya ce gwamnan Kano ya kuma kori shugaban kula da tattara harajin tare da naɗa sabbi a ƙoƙarinsa na sake fasalin tsarin haraji a jihar.

 

Advertisement

Wannan mataki, a cewar sanarwar, zai ƙara inganta ayyukan hukumar wajen tattara haraji a yayin da ake sa ran gwamnan zai gabatar da wani sabon kundi na tattara haraji a jihar a cewar mai magana da yawun gwamnan.

 

Wannan kundi ana sa ran zai magance ƙara inganta karɓar haraji a shekara ta 2025.

 

“Wannan zai taimaka wa gwamnatin wajen cika alkawarin da ta ɗaukar wa al’umma a ɓangarori da dama,” in ji Sunusi Bature.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending