Connect with us

News

Gobara Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Yar Sakataren Gwamnatin Sokoto Da Jikokin Sa 

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

Sakataren Gwamnatin Jihar Sokoto, Alhaji Muhammadu Bello Sifawa, ya rasa ‘yar sa da kuma ‘ya’yan ta guda uku sakamakon wata gobara da ta cinye dukkan gidan su a safiyar Litinin.

Advertisement

Wanda suka rasu sun haɗa da matar Alhaji Muhammadu Yusuf Bello, sakataren dindindin na ma’aikatar wasanni da ci gaban matasa ta Jihar Sokoto.

Yan Sanda Sun Kama Mutum 50 Da Zargin Sace Murafen Kwatami A Kan Tituna

Rahotanni na nuni da cewa wutar ta lalata gidan gaba ɗaya yayin da iyalin suke barci, inda shi kaɗai mijin matar ya tsira.

Advertisement

A lokacin da wakilin Blueprint ya ziyarci wurin, ba a samu tabbacin ainihin sanadin wutar ba, sai dai bincike na ci gaba don gano musabbabin wannan mummunan al’amari.

Jami’an hukumar kashe gobara ta jihar Sokoto sun ɗauki awanni da dama suna yaƙi da wutar kafin su samu nasarar kashe ta.

Advertisement

An gudanar da jana’izar waɗanda suka rasu a masallacin Juma’a na garin Sifawa, cikin ƙaramar hukumar Bodinga, inda aka binne su bisa ƙa’idojin addinin Musulunci.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending