News
An Kai Karar Maigari, Mai Unguwa, Dan Sanda da Limami Bisa Zargin Karɓe Kuɗaɗen Matashi
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Ana tuhumar wasu manyan mutanen gari a ƙaramar hukumar Bagwai da haɗa kai wajen karɓe kuɗaɗen wani matashi Bafulatani da zummar yi masa tara, amma daga bisani suka raba kudin a tsakaninsu.
Mutanen da ake zargi sun haɗa da Maigari, Mai Unguwa, wani ɗan sanda da Limami, waɗanda suka gurfana a babbar kotun shari’ar musulunci da ke Rijiyar Lemo, Kano.
Wanda abin ya shafa, matashi Umar Musa, ya shaida wa wakilinmu Ibrahim Abdullahi Soron Ɗinki cewa an karɓi N130,000 daga gare shi bisa hujjar cewa ya deɓi hatsin ƙaninsa. Amma daga bisani, ƙanin nasa ya bayyana cewa bai damu da ɗiban hatsin ba.
Lamarin na cigaba da ɗaukar hankali, yayin da jama’a ke jiran hukuncin da kotu za ta yanke a kan waɗanda ake zargi da wannan aika-aika.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
