Connect with us

News

Shugaba Tinubu Ya Nemi Majalisar Dattawa Ta Kore Wasu Kwamishinonin Zaɓe

Published

on

Shugaba Tinubu ya bayyana makomar TETFUND da NITDA da NASENI

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN

A yau Laraba, Shugaban Kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, ya nemi amincewar Majalisar Dattawa domin korar wasu kwamishinonin zabe (RECs) na jihohin Abia, Adamawa, da Sokoto da aka dakatar.

Advertisement

Wannan bukata tana kunshe ne a cikin wata wasika da shugaban kasa ya aike wa shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wanda ya karanta a zauren majalisar.

Masarautar Daura Ta Nada Sarautu Ga Wadanda Suka Hidimta Wa AL-QUR’ANI Da Almajirrai

Kwamishinonin zaben da aka dakatar da kuma Tinubu ke neman sallamarsu sun hada da:

Advertisement

Ike Uzochukwu (Abia)

Hudu Yunusa-Ari (Adamawa)

Advertisement

Nura Ali (Sokoto)

Ana zargin wadannan kwamishinoni da aikata rashin da’a da kuma saba ka’idojin aiki a lokacin babban zaben 2023.

Advertisement

Shugaban kasa ya bukaci Majalisar Dattawa da ta amince da sallamar su domin tabbatar da ingantaccen tsarin zabe da rikon amana a harkar gudanar da zabuka a Najeriya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending