Connect with us

News

Gwamnatin Kano Ta Kuduri Aniyar Kawar Da Mace-macen Mata Masu Juna Biyu 

Published

on

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa manufarta ita ce kawar da mace-macen mata masu juna biyu gaba ɗaya, ba ragewa kacal ba.

Advertisement

Kwamishinan Lafiya na Jihar Kano, Dokta Abubakar Labaran Yusuf, ya bayyana haka yayin da yake jawabi a taron Dandalin Haɗin Kan Abokan Haɗin Kai (PCF) da aka gudanar a birnin Kano.

PCF wata sabuwar manufa ce da Kwamishinan ya ƙirƙira domin haɗa duk masu ruwa da tsaki a fannin lafiya, tare da tabbatar da cewa ana aiki bisa tsari guda ba tare da maimaita ayyuka ba.

Advertisement

Ya ce gwamnatin Jihar Kano ta himmatu wajen sauya fannin lafiya, bisa jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda a cikin shekara ɗaya da rabi ya gyara manyan cibiyoyin lafiya da kuma ba da kwangilolin gyaran cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko sama da 200.

Dokta Labaran ya jaddada cewa wannan shiri yana daidai da manufar gwamnati na tabbatar da ingantaccen hidima a cibiyoyin lafiya na matakin farko da na biyu, tare da ba da fifiko ga lafiyar mata da yara, musamman kokarin kawar da mace-macen mata masu juna biyu da jarirai.

Advertisement

Ya bayyana damuwarsa kan kididdigar da ke nuna cewa sama da kashi 70% na mata a Jihar Kano ba sa zuwa asibiti lokacin haihuwa, inda suka fi son haihuwa a gida saboda rashin amincewa da ingancin kulawa a asibitoci.

“A kan haka ne muke gyara asibitocinmu da inganta cibiyoyinmu na matakin farko .

Advertisement

Kwamishinan ya jaddada cewa wannan wani bangare ne na shirye-shiryen gwamnatin Jihar Kano na kawar da mace-macen mata gaba ɗaya.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending