Connect with us

News

Kotu Ta Yanke Hukuncin Shekaru 95 Kan Dillalan Muggan Ƙwayoyi Da Kuɗinsu Ya Kai Biliyan 4.6

Published

on

Kotu ta Yanke Hukuncin Shekaru 95 Kan Dillalan Muggan Ƙwayoyi da Kuɗinsu Ya Kai Biliyan 4.6

DAGA NUSAIBA ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Babbar Kotun Tarayya da ke Lagos da kuma ta Yola, jihar Adamawa, ta yanke hukuncin ɗaurin shekaru 95 a gidan yari kan wasu manyan dillalan muggan ƙwayoyi guda huɗu da aka kama da laifin safarar hodar iblis da darajarta ta kai Naira biliyan 4 da miliyan 600.

Daga cikin waɗanda aka yanke wa hukuncin akwai Ogbuji Christian Ifeanyi, wanda jami’an hukumar NDLEA suka kama tun shekarar da ta gabata a filin jirgin saman Murtala Muhammad da ke Lagos, da hodar iblis ɗauri 817 mai nauyin kilogram 20.

Layin wutar lantarki na Najeriya ya samu tsaiko

Sauran waɗanda aka yanke wa hukuncin sun haɗa da Iloduba Augustine Chinonye, Shuaibu Nuhu Isa (Don) da kuma Zidon Zurga.

Kotun ta kuma umarci ƙwace motoci biyu da aka yi amfani da su wajen safarar ƙwayoyin, tare da biyan tarar Naira miliyan 25.

Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Mohamed Buba Marwa, ya yaba da wannan hukunci da ya ce babban ci gaba ne a yaki da fataucin muggan ƙwayoyi a ƙasar nan.

Advertisement

Sanarwar hukumar na ƙara nuna aniyar NDLEA na ci gaba da tunkarar masu aikata wannan laifi da duk mai hannu a safarar muggan ƙwayoyi a Najeriya.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending