News
An Kama Soja Da Ɗan Sanda Bisa Zargin Satar Batiran Jirgin Ƙasa A Kaduna
An kama wani jami’in soja da wani ɗan sanda mai suna Ajiye Joel bisa Zargin sace batirori daga Hukumar Jiragen Ƙasa ta Ƙasa (NRC), tare da wani jami’in hukumar a Jihar Kaduna.
SAHARA REPORTS ta ruwaito cewa dakarun sojojin atisayen ‘Fansan Yamma’ ne suka cafke su a ranar 19 ga watan Maris. Wannan runduna ta musamman an kafa ta ne domin yaki da ayyukan ta’addanci a Arewa maso Yamma.
A halin yanzu, an tsare su a reshen rundunar sojoji dake Kaduna yayin da ake ci gaba da bincike kan lamarin.
Wannan na zuwa ne bayan wata irin wannan badakala da ta shafi wasu sojoji biyu da aka kora bisa laifin satar wayoyin lantarki a Matatar Dangote, Legas.
-
Opinion5 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion5 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News3 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
