News
‘Yan Sanda Sun Cafke Mutum Biyu Da Wayoyin Sata Na Miliyan 35 A Maiduguri
Rundunar ‘yan sanda ta jihar Borno ta samu gagarumar nasara a kokarinta na yaki da aikata laifuka, inda ta cafke wasu mutane biyu da ake zargi da satar wayoyin hannu na miliyoyin naira a Maiduguri.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana cewa an kama Ba’isa Yerima (25) da Lawan Yusuf (26) dauke da wayoyin hannu guda 61 da kudinsu ya kai Naira miliyan 35.
A cewarsa, an cafke su ne a ranar 15 ga Maris, bayan samun bayanan sirri da suka jagoranci jami’an sashin kula da satar wayoyi zuwa yankin Polo, inda aka kama su da wayoyi da ake zargin sun sata.
Ya kara da cewa daga cikin wayoyin da aka gano, guda bakwai sun kasance cikin rahoton sata, kuma ana ci gaba da kokarin mayar da su ga masu su.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Yusufu Mohammed Lawal, ya jaddada aniyar rundunar na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da yin kira ga duk wanda aka sace masa waya da ya tuntubi rundunar don samun hakkinsa.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
