News
Cutar Sankarau Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutune 3 A Gombe
Gwamnatin Jihar Gombe ta tabbatar da ɓarkewar cutar Ciwon Saman Jijiya (Cerebrospinal Meningitis – CSM) bayan rasuwar mutum uku da kuma tabbatar da wasu 31 da suka kamu da cutar a kananan hukumomi daban-daban.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dr. Habu Dahiru, ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a Cibiyar Agajin Lafiya ta Gaggawa a ranar Alhamis. Ya ce an gano jimillar mutane 70 da ake zargi da cutar a kananan hukumomi tara.
A cewar Dr. Dahiru, daga cikin samfurin ruwa na kwakwalwa (CSF) 63 da aka gwada, 31 sun fito da sakamako mai kyau, inda har yanzu mutum uku suka mutu sakamakon jinkirin kai su asibiti.
Kwamishinan ya bayyana cewa cutar ta wuce matakin annoba a wasu yankuna a Kaltungo, Yamaltu-Deba, da Gombe, wanda ya sa aka ayyana ɓarkewar cutar a hukumance.
“Ina sanar da cewa an samu ɓarkewar cutar CSM a waɗannan yankuna, kuma za mu ci gaba da bayar da sabbin bayanai a yayin da lamarin ke ƙara bayyana,” in ji shi.
CSM cuta ce mai yuwuwar warkewa idan an gano ta da wuri. Alamomin cutar sun haɗa da, Zazzaɓi mai zafi, Matsanancin ciwon kai, Amai, Ciwon wuya, Farfaɗiya, Rikicewar hankali.
Cutar na yaɗuwa ta hanyar rashin tsafta da haɗin numfashi, musamman a wuraren da mutane ke cunkoso.
A halin yanzu, hukumomi na ci gaba da sa ido tare da haɗin gwiwa da Cibiyar Kula da Cututtuka ta Najeriya (NCDC), Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), Médecins Sans Frontières (MSF), da sauran abokan hulɗa don dakile cutar.
