News
Shugaba Tinubu Ya Sauke Mele Kyari, Ya Naɗa Bashir Ojulari a Matsayin Sabon Shugaban NNPC
Shugaban kasa , Bola Ahmed Tinubu, ya sauke Mele Kyari daga shugabancin Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL) a wani gagarumin matakin gyaran kamfanin.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga, ya fitar ranar Laraba, an bayyana cewa an naɗa Bashir Bayo Ojulari a matsayin sabon shugaban NNPC.
Shugaban Tinubu Ya Kore Mele Kyari Daga Mukamin Shugaban NNPCL
Baya ga hakan, Shugaba Tinubu ya yi garambawul ga kwamitin gudanarwar NNPC mai mutum 11, inda Cif Pius Akinyelure ke jagoranta tun bayan naɗa shi a watan Nuwamba na shekarar 2023. A sabon tsarin, Ahmadu Musa Kida zai jagoranci kwamitin gudanarwar kamfanin.
Mele Kyari ya hau shugabancin NNPC a shekarar 2019, lokacin mulkin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, bayan ritayar Maikanti Baru. Wannan sauyin shugabanci na daga cikin matakan da gwamnatin Tinubu ke dauka domin sake fasalin harkokin man fetur a Najeriya.
-
News1 day ago
Ana Zargin Matar Aure Da Shaƙe ’Yar Kishiyarta Mai Shekara 3 Har Lahira
-
News19 hours ago
Ba Za Mu Yi Wa Kowa Rangwame Ba A Wajan Yaƙi Da Sha Da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi Ba — Muhyi Magaji
-
News6 days ago
KANO: Yara 24 Da Ake Tuhuma Da Laifi Sun Amfana Da Shirin Gyaran Tarbiya Maimakon Hukuncin Kotu A Watan Yuli
