Connect with us

News

Kisan Edo: Jami’an Hukumar DSS Sun Kama Manyan Mutane Biyu Da Ake Zargi

Published

on

Dss

Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) sun cafke wasu manyan mutane biyu da ake zargi da hannu wajen kisan matafiya 16 da aka yi a Uromi, karamar hukumar Esan Arewa maso Gabas ta jihar Edo a makon jiya.

Sanarwar da Babban Sakataren Yada Labarai na gwamnan jihar, Friday Ituah, ya fitar a ranar Talata ta tabbatar da kamen, inda ya ce an kama su ne bisa sahihan bayanan sirri.

Advertisement

Shugaba Tinubu Ya Sauke Mele Kyari, Ya Naɗa Bashir Ojulari a Matsayin Sabon Shugaban NNPC

A cewarsa, jami’an tsaro na ci gaba da farautar wasu da ake kyautata zaton suna da alaka da wannan aika-aika. Hukumomin tsaro sun garzaya da wadanda aka kama zuwa Abuja don ci gaba da bincike da shirin gurfanar da su a gaban shari’a.

 

Advertisement

A ranar Litinin, Gwamnan Edo, Sanata Monday Okpebholo, ya kai ziyarar jaje jihar Kano ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu. Ya bayyana cewa an kama mutum 14 da ake zargi da hannu a lamarin, kuma dukkansu za a kai Abuja don karin bincike.

Gwamnan ya tabbatar wa iyalan wadanda abin ya shafa cewa gwamnati za ta tabbatar da adalci, tare da biyan diyya ga iyalan da suka rasa ‘yan uwansu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending