News
FASAHAR ZAMANI DA KARATUN LITTATTAFAI: Masana Sun Fadi Yadda Fasahar Zamani Ke Rage Sha’awar Karatu
A ranar Asabar, 24 ga Mayu, 2025, wani taron tattaunawa mai muhimmanci ya gudana a Jami’ar Khalifa Isyaku Rabi’u da ke Kano, inda masana biyu daga Jami’ar Bayero Kano suka yi bayani game da yadda fasahar zamani ke shafar sha’awar karatu.
Taron, wanda kungiyar D-E-E-D-S Dialogue Debate International ta shirya, ya samu halartar dalibai, malamai, likitoci, injiniyoyi, lauyoyi da sauran jama’a masu sha’awar ci gaban ilimi. Taken tattaunawar shi ne: “Books vs. Screens: Has the Digital Age Killed the Love for Reading?” Wato, shin zamanin dijital ya sa mutane sun daina son karatun littattafai?
Kwamitin Zaman Lafiya Na Kano Ya Yi Kira Da A Yi Bukukuwan Sallah Cikin Natsuwa Da Zaman Lafiya
Wadanda suka yi magana
Farfesa Ibrahim Bello Kano (IBK) daga Sashen Turanci, Jami’ar Bayero Kano
Dr. Bala Muhammad, masani a fannin Harkokin Watsa Labarai daga wannan jami’a
Farfesa Abdalla Uba Adamu, tsohon shugaban Jami’ar NOUN, shi ne ya jagoranci taron. Ya ce wannan tattaunawar ba muhawara ce ta jayayya ba, amma dai don fitar da gaskiya da ra’ayoyi masu amfani.
Me Masana Suka Ce?
Farfesa IBK ya yi bayani cewa karatu abu ne da ake koya, ba wai yana zuwa da kansa ba. Ya ce fasahar zamani irin ta wayar hannu da intanet ta janyo hankalin matasa daga littattafai zuwa kafafen sada zumunta, inda ba sa samun karuwar sha’awar karatu.
Dr. Bala Muhammad ya bayyana cewa fasahar zamani ta sauƙaƙa yadda mutane ke samun bayanai, musamman matasa da ke amfani da na’urori kamar waya da kwamfuta. Amma kuma ya ce akwai bukatar a daidaita tsakanin karatun gargajiya da na zamani domin samun ilimi mai kyau.
Dukkaninsu sun nuna damuwa kan yadda wasu kafafen sada zumunta, musamman TikTok, ke yada abubuwan da ba su da amfani ga tarbiyyar matasa.
Taron ya gudana cikin lumana da kwanciyar hankali, inda kowa ya saurari bayanan masana da natsuwa. An nuna godiya ga yadda aka shirya komai yadda ya kamata, kuma an jaddada muhimmancin irin wannan taron domin ilmantar da jama’a.
Dr. Abdussalam Sani daga Jami’ar Aliko Dangote, Wudil, ya yaba da rawar da kowa ke takawa wajen ilmantar da al’umma
Masana sun roki iyaye, malamai da shugabannin al’umma su taimaka wajen dawo da sha’awar karatu, musamman ga matasa. Sun ce karatu na taimakawa wajen gina tunani mai kyau da rayuwa mai inganci.
Wannan taro shi ne na farko daga jerin wasu da kungiyar D-E-E-D-S za ta ci gaba da shirya a makonni masu zuwa.
