Connect with us

News

Ƙudirin Dokar Hana Jami’an Gwamnati Amfani Da Asibitoci Da Makarantun Kuɗi Ya Tsallake Karatun Farko

Published

on

images 3 3

Majalisar Wakilai ta fara duba wani kudiri da ke neman hana jami’an gwamnati da iyalansu amfani da asibitocin kuɗi da makarantun masu zaman kansu a Najeriya.

Ɗan majalisar da ya gabatar da kudirin, Hon. Amobi Ogah, mai wakiltar mazaɓar Isuikwuato/Umunneochi daga Jihar Abia, ya ce an tsara dokar ne domin tilasta wa jami’an gwamnati amfani da cibiyoyin gwamnati.

Advertisement

Ƙauyuka 739 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa A Najeriya ‎ —NIHSA ‎ ‎

A yayin da ya ke bayyana manufar kudirin, Hon. Ogah ya ce makasudin hakan shi ne farfaɗo da asibitoci da makarantun gwamnati da kuma rage yawan kuɗin da ake ɓarna da su wajen neman magani ko ilimi a waje.

“Yanzu haka cibiyoyinmu na lafiya da ilimi suna fama da matsaloli da dama saboda shugabanni ba sa amfani da su. Maimakon haka, suna tura ’ya’yansu zuwa makarantun masu tsada a cikin gida da ƙasashen waje, sannan su kan je ƙasashen waje domin neman magani,” in ji shi.

Advertisement

Ya ce idan har an tilasta wa shugabanni amfani da makarantun da asibitocin gwamnati, hakan zai sa su fara kulawa da su domin suna da muradin amfana da ingancinsu kamar sauran ’yan ƙasa.

Majalisar dai ta karanta kudirin a matakin farko a zaman da aka gudanar ranar Talata, kuma ana sa ran ci gaba da nazari a matakai na gaba kafin a yanke hukunci a kansa.

Advertisement

 

 

Advertisement

BLUEPRINT

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending