News
Gobara Ta Ƙone Rumfuna Sama Da 500 A Kano
Rahotanni daga jihar Kano na cewa, gobara ta tashi a kasuwar Shuwaki da ke cikin ƙaramar hukumar Gari, inda ta ƙone rumfuna sama da 500 kurmus.
Mai magana da yawun Hukumar kashe gobara ta Jihar Kano, ACFO Saminu Yusuf Abdullahi, ya tabbatar da faruwar lamarin a wani jawabi da ya fitar, inda ya ce wutar ta tashi ne da misalin ƙarfe 3:25 na rana a ranar Laraba.
Hare-haren ’Yan Bindiga Ya Fara Ƙamari A Yankin Shanono, Jihar Kano
A cewar Abdullahi, hukumar ta samu kiran gaggawa daga kwamandan Hukumar na Gari, Abdulmalik Muhammad, wanda ya sanar da tashin wutar.
Ya ce, “Daga nan ne tawagar jami’an Hukumar daga ofishin Danbatta suka isa wurin don kashe wutar. Da isarsu, sun tarar da kasuwar — wacce ke da fadin kusan kafa 3,000 zuwa 2,500 da rumfuna fiye da 1,000 — tana ci da wuta. Akalla rumfuna 529 ne suka ƙone gaba ɗaya.”
Sai dai babu rahoton asarar rai a lamarin.
-
Opinion7 days ago
Ayyuka, Bin Diddigi, Biyan Kudi, Sakamako: Dabarun Kano Da Suka Zarce Jihohi 35
-
Opinion7 days ago
Tiriliyan ₦210 na Karya: Yadda Bala Wunti Ya Warware Dukkan Rudanin da Ya Mamaye Zaman Majalisar Dattawa Kan Asusun NNPC
-
News5 days ago
Likitan El-Rufai Ya Shiga Matsala Kan Zargin Bayar Da Rahoton Jinya Na Bogi
