News
Wani Saurayi Ya Kashe Abokinsa Saboda Rikici Kan Budurwa
Wani saurayi mai shekaru 25, Hammed Usman Tunde, ya rasu bayan abokinsa, Gafar mai shekaru 21, ya soka masa wuƙa a kirji. Lamarin ya faru ne a unguwar Oja Gboro, babban birnin jihar Kwara, sakamakon rikici da suka yi kan wata budurwa.
Rahotanni daga wurin sun bayyana cewa rikicin ya fara ne a wajen mai sayar da rake, inda suka fara muhawara wadda ta kai ga tashin hankali. A lokacin, Gafar ya caka wa Tunde wuƙa a kirji.
Kwamishinan Shari’a Na Kano Ya Halarci Taron Nahiyar Afrika Kan Yaƙi Da Safarar Mutane A Legas
An garzaya da Tunde asibiti, inda daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa. Mamacin ya kasance mazaunin Ile-Soro 2, Isale Koko, Oja Gboro.
Advertisements
