News
Gwamnatin Kano Ta Tabbatar Da Ɓullar Cutar Shan Inna
Hukumar kula da lafiya a matakin farko ta jihar Kano ta tabbatar da gano sababbin nau’o’i guda huɗu na ƙwayar cutar shan inna a jihar, tare da gargaɗin cewa idan ba a ci gaba da yin rigakafin yadda ya kamata ba, kwayar cutar na iya sake yaɗuwa bayan an kawar da ita.
Farfesa Salisu Ahmad, wanda Daraktan hukumar ya wakilta ne ya bayyana hakan yayin taron tattaunawa da jama’a domin tunawa da Ranar Polio ta Duniya a Kano, a ranar Laraba.
Bamu Da Cikakkun Kayan Aikin Yaƙi Da Ƴan Ta’adda —Babban Hafsan Soji Najeriya
Ya ce tsakanin shekarun 2013 zuwa 2015, Kano ce cibiyar yaɗuwar cutar a Najeriya, amma sakamakon hadin gwiwar gwamnatin jihar da abokan hulɗa, an samu nasarar kawar da ita.
Sai dai ya bayyana cewa aikin bai ƙare ba, domin an sake gano sababbin nau’o’i hudu na ƙwayar cutar, inda har yanzu ana binciken ɗaya daga cikinsu a ɗakin gwaje-gwaje.
Da take bayani kan halin da ake ciki game da cutar shan inna a jihar, Jami’ar Rigakafi ta Jihar, Hajiya Sa’adatu Ibrahim, ta ce an gano sabbin nau’o’i biyu na ƙwayar cutar a wajen yara da ke yankunan karkara, yayin da sauran biyun kuma an gano su ne a cikin ruwan da ya gurɓace a wasu yankuna na birni.
“Tsabtace muhalli shi kaɗai bai wadatar wajen kawar da cututtukan da ake iya hana su ta rigakafi ba. Dole ne mu ci gaba da tabbatar da cewa ana yi wa ’ya’yanmu allurar rigakafi,” in ji ta.
“Dole mu kasance cikin shiri don tabbatar da cewa an kawar da cutar shan inna gaba ɗaya,” in ji jami’ar.
BBC HAUSA
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
