Connect with us

News

Shugabar Tanzania Ta Bai Wa Sirikinta Da ’Yarta Muƙamin Minista

Published

on

images

Shugabar Tanzania, Samia Suluhu Hassan, ta sanar da sabon jerin ministocinta, inda ta ƙirƙiri sabuwar Ma’aikatar Matasa kuma ta ƙara adadin ma’aikatun gwamnati zuwa 27.

A cikin sabbin naɗe-naɗen da ta yi, ta naɗa ’yarta, Wanu Hafidh, a matsayin ƙaramar ministar ilimi, sannan ta naɗa sirikinta, Mohamed Mchegerwa, a matsayin ministan lafiya.

Advertisement

Kotu Ta Yanke Wa Farfesa Hukuncin Shekaru 5 A Gidan Yari

Gwamnatin Sin Ba Ta Taba Bukatar Kamfanoni Su Tattara Ko Adana Bayanai Ba Bisa Ka’ida Ba Kuma Ba Za Ta Yi Hakan Ba

Shugabar ta sake dawo da wasu tsofaffin ministoci guda bakwai, amma ta cire tsohon mataimakin firaminista, Dotto Biteko, da tsohuwar shugabar majalisa, Tulia Ackson.

Advertisement

Sabbin naɗe-naɗen na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da Shugaba Samia ta kafa kwamitin bincike kan zanga-zangar bayan zaɓe, inda jam’iyyun hamayya da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam suka zargi jami’an tsaro da kashe mutane da dama.

Duk da haka, hukumomi ba su bayyana adadin waɗanda suka rasu ba.

Advertisement

Shugabar ƙasar ta lashe zaɓen ne da kashi 98 na ƙuri’un da aka kaɗa.

 

Advertisement

 

LEADSHIP HAUSA 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending