Connect with us

News

Gwamnatin Kano Za Ta Hukunta Duk Wanda Aka Samu Na Amfani Da Babur Mai Kafa 2 Da Nufin Achaba

Published

on

2020 01 28t120259z 1454570781 rc20pe91aekh rtrmadp 3 nigeria english 0

Gwamnatin Jihar Kano ta ce za ta hukunta duk wani mutum da aka kama yana gudanar da sana’ar achaba a cikin birnin Kano da kewaye, duk da haramcin da aka dade da kakabawa wannan kasuwanci.

‎Hakan na zuwa ne bayan da rahotanni suka nuna cewa masu babur mai kafa biyu sun fara sake bayyana a titunan Kano, lamarin da ya haifar da ƙarin damuwa a tsakanin jama’a da hukumomi.

Advertisement

Sanata Barau Da Harkar Tsaro

‎A cikin wani saƙon manema labarai da Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta jihar ta fitar, gwamnatin ta tabbatar da cewa rahotannin leƙen asiri sun nuna akwai yawaitar masu babur, har ma da wasu mutane ba a san su ba da ke shigowa unguwanni suna zirga-zirga da babura da sunan achaba.

‎Gwamnatin ta ce an tura ƙarin jami’an tsaro domin dakile wannan matsala a kananan hukumomi 44 na jihar.

Advertisement

‎ “Duk wanda aka kama yana yin achaba a Kano, babu shakka zai fuskanci hukuncin doka.”

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending