Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Wajabta Gwajin Ta’ammali Da Muggan Ƙwayoyi Ga Masu Neman Aikin Gwamnati

Published

on

Tinubu

Gwamnatin Tarayya ta umarci dukkan ma’aikatu, hukumomi da sassan gwamnati su sanya gwajin miyagun ƙwayoyi a matsayin sharadi na wajibi kafin ɗaukar sabbin ma’aikata aiki.

Umarnin ya fito ne daga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, inda aka bukaci hukumomin gwamnati su yi aiki tare da Hukumar Yaƙi da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) domin gudanar da gwaje-gwajen bisa ƙa’idoji.

Advertisement

An Sace Mutane 28 A Hanyarsu Ta Zuwa Maulidi A Filato

Gwamnatin ta ce matakin na da nufin rage yawaitar shan miyagun ƙwayoyi, musamman a tsakanin matasa, tare da kare lafiyar jama’a, inganta nagartar aiki, bunƙasa tattalin arziki da ƙarfafa tsaron ƙasa.

Wannan mataki na cikin jerin manufofin yaƙi da miyagun ƙwayoyi na shekarar 2025 da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa.

Advertisement

A baya-bayan nan, wasu hukumomi kamar Hukumar Kwastam ta Najeriya, da kuma wasu jami’o’i, sun fara aiwatar da gwajin miyagun ƙwayoyi ga sabbin ma’aikata da ɗalibai, a wani yunƙuri na ƙasa baki ɗaya na magance matsalar.

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending