Connect with us

News

Dan Majalisar Jiha Na Ungogo Aminu Sa’ad Ya Rasu

Published

on

IMG 20251224 WA00771

Ɗan Majalisar Dokokin Jihar Kano mai wakiltar Karamar Hukumar Ungogo, Aminu Sa’adu Ungogo, ya rasu a Kano.

Mai magana da yawun Majalisar Dokokin Jihar Kano, Kamaludeen Sani Shawai, ya tabbatar da rasuwar ɗan majalisar , inda ya ce marigayin ya kamu da gajeriyar rashin lafiya jim kaɗan bayan ya  isa Majalisar Dokoki.

Advertisement

A cewar Shawai, an garzaya da Aminu Sa’adu zuwa asibiti domin samun kulawar gaggawa, amma daga bisani likitoci suka tabbatar da rasuwarsa da yammacin ranar.

Ya ƙara da cewa za a gudanar da sallar jana’izar marigayin da misalin ƙarfe 6 na yamma a ranar Talata.

Advertisement

Rasuwar Aminu Sa’adu ta haifar da jimami a Majalisar Dokokin Jihar Kano da kuma Karamar Hukumar Ungogo, inda abokan aikinsa da ‘yan mazabarsa ke bayyana alhini kan rasuwar ɗan majalisar, wanda ya kasance mai wakiltar yankinsa a zauren majalisar jihar.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending