Connect with us

News

Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Kashe Jariri A Kano 

Published

on

kotu
Spread the love

Babbar Kotun Jihar Kano, karkashin Mai Shari’a Aisha Yau, ta yanke wa Abubakar Alhaji Sabo hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe jaririn da ya haifa tare da budurwarsa.

Gwamnatin Jihar Kano ta gurfanar da Abubakar Sabo a gaban kotu kan laifin kisan kai .

Cin Awara Na Taimakawa Wajen Rage Hawan Jini  —Likita

Wanda ake tuhuma ya haifi jaririn  ba tare da aure ba , sannan ya yi yunkurin kashe shi saboda budurwar ta ƙi bin umarninsa.

Advertisement

An kuma same shi da laifin tada rikici ga mahaifiyar jaririn lokacin da aka same shi yana bai wa jaririn fiya-fiya.

A shari’ar, Barista Safiya Yalwati Yahaya, mai gabatar da ƙara, ta gabatar da shaidu uku, yayin da wanda ake ƙara ya kare kansa.

Bayan nazarin hujjojin bangarorin biyu, kotun ta same shi da laifin kisan jariri, ta yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya, sannan ta ƙara masa hukuncin shekaru uku ɗaurin gidan yari saboda haddasa rauni.

Advertisement

 

DAILY POST 

Advertisement
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *