News
Mutane A Kauyen Jagalari Sun Nakasta Wani Da Ake Zargi Barawon Dabbobi Ne
Mutane a kauyen Jagalari da ke Karamar Hukumar Fune a Jihar Yobe, sun nakasta wani da ake zargi barawon dabbobi ne
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne da misalin karfe 1:30 na dare, lokacin da matasan biyu Manu Ja’oji mai shekara 20 da Kabo Shungel, dukkansu daga kauyen Tashan Fulani a Karamar Hukumar Tarmuwa, suka shiga Jagalari da nufin satar dabbobi.
ICPC Ta Gurfanar Da Na Hannun Daman El-rufai A Kotu Kan Zargin Sama Da Faɗi Da Naira Biliyan 311
Shedun gani da ido sun ce al’ummar garin sunyi arangama dasu, lamarin da ya sa Manu Ja’oji ya jikkata sosai, yayin da abokin nasa ya tsere.
Jami’an tsaro sun garzaya wurin, tare da kai wanda ya jikkata Asibitin Babangida, daga bisani aka mika shi Asibitin Kwararru na Damaturu domin ci gaba da jinya.
Yanzu haka ana ci gaba da bincike tare da neman wanda ya tsere.
