News
Ydda Mutane Suka Je Ɗiban Ganima Bayan Faɗuwar Tankar Man Fetur A Ibadan
wani sabon bidiyo ya sake nuna yadda wasu mutane ke ci gaba da jefa rayukansu cikin hadari yayin da suke kwasar man fetur daga tankar da ta yi hatsari.
RahotanniRahotanni daga birnin Ibadan sun ce wasu mazauna yankin sun taru a kan titin Academy zuwa Iwo Road, inda wata tankar mai ta kife, suka fara dibar man fetur duk da barazanar tashin gobara ko fashewa.
Wata Mata Ta Haifi ’Yan Huɗu Lokaci Guda A Ogun
Bidiyon da aka wallafa a ranar Lahadi ya nuna jama’a na cika galan da kwantena da mai, ba tare da la’akari da hadarin da ke tattare da irin wannan aiki ba.
Hukumomi sun dade suna gargadi kan wannan dabi’a, wadda ke yawan janyo asarar rayuka a fadin Najeriya.
A cewar Hukumar FRSC akalla mutane 411 ne suka mutu a shekarar 2024 sakamakon irin wadannan lamurra.
Ko a farkon shekarar 2026 ma, an sake samun irin wannan lamari a yankin Apapa, inda wata tankar dizal ta kife, jama’a suka fara kwasar mai kafin jami’an agaji su iso wurin.
Hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Legas ta gargadi al’umma da su guji kusantar tankunan da suka yi hatsari, tana mai cewa hakan na iya haddasa mummunar gobara cikin gaggawa.
Hukumomi na ci gaba da jan hankalin ‘yan Najeriya da su fifita tsaron rayukansu, suna mai jaddada cewa neman riba ta wucin gadi bai kamata ya kai ga rasa rai ba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
