News
Akwai Yiwuwar Ƙara Kuɗin Kiran Waya Da Aika Saƙo A Najeriya
Hukumar kula da sadarwa ta Najeriya ta fara nazari akan kuɗaɗen da ake biya wajen kira da aikewa da saƙonnin kar-ta-kwana a ƙasar, shekaru 8 bayan da aka ƙara kuɗin.
Da yake jawabi a wurin taron tattaunawa na masu ruwa da tsaki kan kayyadewa da daidaita farashin sada abokan hulɗa masu amfani da layukan lamfanoni mabanbanta na wayoyin salula, wanda aka gudanar a Lagos a wannan Talata, wani babban jami’i a kamfanin KPMG, Wole Adenekan, ya ce idan farashin ya yi kasa sosai, ba zai nuna ainihin kudin da ake kashewa wajen samar da hidimar sadarwar ba, kuma zai iya kashe ƙwarin gwiwar masu zuba jari a ɓangaren samar da ababen more rayuwa.
Gwamnatin Tarrayya Ta Musanta Shirin Soke NBAIS
Adenakan ya kuma ƙara da cewa hukumar kula da sadarwa ta Najeriya na sake nazari akan wannan farashi da zummar yin abin da ya dace.
Farashin jona sadarwa ko kuma Mobile Termination Rate, shi ne farashin da kamfanin sadarwa ke biyan wani kamfanin yayin da abokin cinikinsa ya yi kira kuma aka karɓa a wata hanyar sadarwa ta daban.
Shi ne tsarin farashin da ke haɗa kowane mai amfani da layin wayar hannu na Najeriya, ba tare da la’akari da kamfanin sadarwarsa ba, ko kuma wane abokin hulɗa ne ke kira ba.
A yanzu farashin da ake caji ya kai ₦3.90 a kowane minti guda zuwa ₦4.70.
Idan har aka sake ƙara farashin a nan gaba, masu amfani da wayoyin sadarwa a ƙasar za su biya ƙarin kuɗi don yin kira da aikewa da saƙon kar-ta-kwana wato SMS.
-
News4 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News5 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News5 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
