News
An Dakata Da Aikin Titin Abuja-kano Saboda Rashin Tsaro Inji Gwamnatin Tarayya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin tarayya, ta ce gyaran hanyar Abuja zuwa Kaduna da Kano da ake yi ya tsaya ne sakamakon barazanar da ake fuskanta ta rashin tsaro a yankin arewa.
Karamin Ministan ayyuka da gidaje Umar Ibrahim El-Yakub yay a bayyana haka, yayin da ya duba wani aikin titi a Kaduna, inda ya ce an tsaida aikin ne bayan harin da aka kai wa jirgin kasa daga Abuja zuwa Kaduna.
Tankar Mai Ta Fadi A Babban Hanyar Lagos Zuwa Ibadan
A wata sanarwa daraktar yada labarum sa Blessing Lere-Adams ta fitar, ta ce akasin abin da mutane ke cewa an yi watsi da aikin ba haka lamarin yake ba, an dakatar da aikin ne kuma za a cigaba.
Daraktar ma’aikar ayyuka da gidaje, ta ce ba da dadewa ba za a cigaba da aikin titin Abuja zuwa Kaduna da Kano domin an samu tsaro a halin yanzu.
Mutane da dama dai na fargabar irin wannan matakan, ka iya jawo tsaiko ne game da aikin.
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
-
News5 days ago
Kwamitin Tsara Kundin Yakin Neman Zaɓen Gwamnan Kano Ya Yi Taron Tsare-tsare Manufofin Ci Gaban Jihar A Kaduna
