News
Uba Ya Karya Hannun Jaririnsa Mai Wata 2 Saboda Kuka
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wani magidanci ya lakada wa jaririn dansa mai wata biyu da haihuwa duka, har ya karya masa hannu saboda ya hana shi barci.
Dukan kawo wukan ya karya hannun daman jaririn tare da yi masa mummunan rauni wadanda suka yi sanadiyar yanke hannun a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Owerri, Jihar Imo.
An Dakata Da Aikin Titin Abuja-kano Saboda Rashin Tsaro Inji Gwamnatin Tarayya
Magidancin ya yi amfani da hangar rataye kaya ne ya rika jibgar jaririn, saboda kukan da yake tsalawa ya hana shi barci.
Hukumar Kare Hakkin dan Adam ta Kasa (NHRC) tabukaci Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Imo ta cafke mutumin, da ya yi jaririnsa mai wata biyu da haihuwa wannan aika-aika.
Hukumar ta yi kiran ne tare da da kungiyar Mata Yan Jarida (NAWOJ) da mahaifar jaririn, suna masu neman a kwato masa hakkinsa daga wannan rashin imani da mahaifinsa ya nuna masa.
Shugabar NAWOJ Reshen Jihar Iko, Dokta Dorothy Nnaji wadda ta ziyarci jaririn da mai jegon a asibiti ta ce shekarun mahaifin yaron 31 kuma dan asalin kauyen Amiril da ka Karamar Hukumar Isu ta jihar ne.
AMINIYA
-
News2 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News5 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
-
News5 days ago
Kwamitin Tsara Kundin Yakin Neman Zaɓen Gwamnan Kano Ya Yi Taron Tsare-tsare Manufofin Ci Gaban Jihar A Kaduna
