Connect with us

News

Uba Ya Karya Hannun Jaririnsa Mai Wata 2 Saboda Kuka

Published

on

Wata jaririya

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wani magidanci ya lakada wa jaririn dansa mai wata biyu da haihuwa duka, har ya karya masa hannu saboda ya hana shi barci.

 

Advertisement

Dukan kawo wukan ya karya hannun daman jaririn tare da yi masa mummunan rauni wadanda suka yi sanadiyar yanke hannun a Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Owerri, Jihar Imo.

 

Advertisement

An Dakata Da Aikin Titin Abuja-kano Saboda Rashin Tsaro Inji Gwamnatin Tarayya

Magidancin ya yi amfani da hangar rataye kaya ne ya rika jibgar jaririn, saboda kukan da yake tsalawa ya hana shi barci.

Advertisement

 

Hukumar Kare Hakkin dan Adam ta Kasa (NHRC) tabukaci Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Imo ta cafke mutumin, da ya yi jaririnsa mai wata biyu da haihuwa wannan aika-aika.

Advertisement

 

Hukumar ta yi kiran ne tare da da kungiyar Mata Yan Jarida (NAWOJ) da mahaifar jaririn, suna masu neman a kwato masa hakkinsa daga wannan rashin imani da mahaifinsa ya nuna masa.

Advertisement

 

Shugabar NAWOJ Reshen Jihar Iko, Dokta Dorothy Nnaji wadda ta ziyarci jaririn da mai jegon a asibiti ta ce shekarun mahaifin yaron 31 kuma dan asalin kauyen Amiril da ka Karamar Hukumar Isu ta jihar ne.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

AMINIYA

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending