Connect with us

News

Ruwa Ya Ci Matasa ’Yan Makaranta 2 A Zariya 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Wasu matasa biyu, ’yan aji daya a karamar Sakandaren Gwamnati da ke Zariya a Jihar Kaduna, sun nitse a ruwa a lokacin da suke ninkaya a Kogi.

 

Advertisement

Matasan da suka gamu da ajalin nasu sune Zakariya Aliyu Yahaya da Yusuf Abdullahi, masu shekaru 17 da 16.

 

Advertisement

Kudin da aka ware don yaki da labaran ƙarya sun yi kadan – Lai Mohammed

Wani abokinsu mai suna Musa Dogara ne ya bayyana rasuwar matasan a Angwar Sirdi a Zariya, inda ya c, “Bayan faduwar rana ne ba su dawo ba, sai muka fara nemansu, nan take wani abokinsu ya sanar da mu cewa sun tafi wanka kogi.”

Advertisement

 

Iyayensu sun bayyana cewar tun da sun fara yin hankalin kansu, ba su damu da inda suka shiga ba sai dai aka kwana daya ba tare da an ji duriyarsu ba sannan aka shiga nemansu.

Advertisement

 

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, DSP Mohammed Jalige bai tabbatar da faruwar lamarin ba.

Advertisement

 

Amma ya ce za su bincika da zarar sun samu wani bayani, za su yi wa manema labarai karin haske.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending