News
Ruwa Ya Ci Matasa ’Yan Makaranta 2 A Zariya
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu matasa biyu, ’yan aji daya a karamar Sakandaren Gwamnati da ke Zariya a Jihar Kaduna, sun nitse a ruwa a lokacin da suke ninkaya a Kogi.
Matasan da suka gamu da ajalin nasu sune Zakariya Aliyu Yahaya da Yusuf Abdullahi, masu shekaru 17 da 16.
Kudin da aka ware don yaki da labaran ƙarya sun yi kadan – Lai Mohammed
Wani abokinsu mai suna Musa Dogara ne ya bayyana rasuwar matasan a Angwar Sirdi a Zariya, inda ya c, “Bayan faduwar rana ne ba su dawo ba, sai muka fara nemansu, nan take wani abokinsu ya sanar da mu cewa sun tafi wanka kogi.”
Iyayensu sun bayyana cewar tun da sun fara yin hankalin kansu, ba su damu da inda suka shiga ba sai dai aka kwana daya ba tare da an ji duriyarsu ba sannan aka shiga nemansu.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, DSP Mohammed Jalige bai tabbatar da faruwar lamarin ba.
Amma ya ce za su bincika da zarar sun samu wani bayani, za su yi wa manema labarai karin haske.
-
News18 hours ago
Jam’iyyar Labour Party Ta Yi Alkawarin Kafa Hukumar Kula Da Hayar Gidaje A Kano
-
News3 days ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
