News
‘Bam’ Ya Kashe Mutum 2 A Kaduna
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu mutum biyu sun mutu yayin da wani abu da aka binne ya fashe ya kuma tashi da su a Karamar Hukumar Chikun ta jihar Kaduna.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 2:00 na yammacin Alhamis.
Mun Lalata Haramtattun Matatun Mai Sama Da 70 Cikin Mako 2 – Sojoji
Motar wadanda abin ya rutsa da su ta bi ta kan abin fashewar da ake zargin ’yan ta’adda ne suka dasa a Zangon Tofa a yankin Kabrasha.
Aminiya ta rawaito cewa mutanen kauyen na jigilar amfanin gonar da suka girbe lokacin da lamarin ya afku.
Kwamishinan Tsaro da Al’amuran Cikin Gida na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya ayyana mutum biyu a matsayin wadanda suka rasa rayukansu; Babajo Alhaji Tanimu da Safiyanu Ibrahim.
A cewarsa, Gwamnatin Jihar na bincike kan lamarin.
Ya kuma ce Gwamnan Jihar, Nasiru El-Rufai, ya jajanta wa iyalan wadanda abin ya shafa.
-
News4 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News6 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News5 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
