News
Ana fargabar mutuwar mutane da dama bayan da ruwa ya tafi da gidajensu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Ana fargabar mutane da dama sun mutu bayan ruwa yayi awon gaba da gidajensu sakamakon mamakon ruwan sama a tsiburin Ischia na ƙasar Italiya.
An ga ɓaraguzan gine-gine da bishiyoyi da kananan motoci tare da sauran tarkace ruwa na gudu da su cikin kogi a ranar Asabar.
Ranar Litinin Za A Dawo Da Sufurin Jirgin Kasan Abuja-Kaduna – Gwamnati
Wata mace mai shekara 25 tare da iyalanta ciki har da sabon jaririnta na daga cikin waɗanda rahotonni ke cewa sun ɓace.
Magajin garin Lacco Ameno ɗaya daga cikin garuruwan da ke tsiburin, ya ce har yanzu ba a san inda gomman iyalai suke ba, yayin gine-gine da dama suka ruguje. Haka kuma rahotonni sun ce mutane da dama na maƙale a cikin wani otal da ke tsiburin.
An dai yi gargaɗin cewa yanki zai fuskanci mamakon ruwan sama haɗe da iska mai ƙarfi har zuwa ranar Lahadi.
Jami’an yankin sun umarci mazauna tsiburin da su zauna a gidajensu, domin kauce wa rashin samun taimakon gaggawa idan buƙatar hakan ta taso.
