News
An sanya ranar fara rijistar jarrabawar JAMB ta 2022
Daga kabiru basiru fulatan
Hukumar shirya jarrabawa shiga manyan makarantu ta ƙasa (JAMB) ta sanya ranar da za a fara rijistar jarrabawar.
Kakakin hukumar mai suna Dr Fabian Benjamin, ya ce za a fara rijistar ne a ranar 12 ga Fabarairu zuwa 19 ga Maris na 2022.
Hukumar ta sanar da wannan ne ta takardun sanarwa da take fitarwa, na ranar Litinin 24 ga Janairun wannan shekarar.
Advertisements
