Connect with us

News

Yansanda Sun Kubutar Da Mutum Hudu Daga Masu Garkuwa A Kano

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta ce, ta samu nasarar kubutar da mutum hudu daga hannun masu garkuwa da kuma kama mutum 17 da ake zargi da hannu dumu-dumu a wajen aikata laifin.

 

Advertisement

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya bayyana haka a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Kano.

 

Advertisement

Yan sandan Jamus sun gano kayan tarihin da aka sace na dala miliyan 119

Ya ce, an kama wadanda ake zargin da laifin garkuwa da mutane har sau uku cikin wata daya, sakamakon kokarin da rundunar ‘yansandan jihar Kanon ke yi na kakkabe bata-gari daga cikin al’umma.

 

Advertisement

Kamar yadda daya daga cikin wadanda aka Kaman ya ce, abu na farko ya faru ne lokacin da wata motar haya ke tawo wa daga karamar hukumar Funtuwa, ta nufi jihar Kebbi, wasu masu garkuwa suka kama shi, suka rike shi, har tsawon kwana 12; sai da aka biya kudin fansa sannan suka sake shi.

 

Advertisement

An kama wanda wadanda ake zargin ne a tashar Rijiyar Zaki, da ke Kano, lokacin da suke kokarin hawa mota su gudu Faskari.

SP Kiyawa ya ce, yanzu haka suna ci gaba da bincike, kuma suna samun bayanai da za su taimaka musu wajen kamo sauran wadanda ke da hannu a kan wannan laifin.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Aboda haka, sai kwamishinan ‘yansandan jihar Kano, CP Mamman Dauda, ya bukaci al’umma sy ci gaba da ba su hadin kai domin ganin an kawo karshen masu aikata miyagun laifuka a fadin jihar ta Kano.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending