News
Gobara Ta Kone Gidan Kwamishina
DAGA MARYAM BASHIR MUSA
Gobara ta kone gidan Kwamishinan Harkokin Gona na Jihar Ogun a ranar Alhamis.
Iftila’in ya faru ne a yankin Kemta Idi-Aba da ke Abeokuta, babban birnin jihar.
Ya zuwa hada wannan labari ba a samu cikakken bayani ba kan dalilin aukuwar gobarar.
Kwamishinan, Dokta Odedina shi ne wanda ya tabbatar da aukuwar gobarar, inda ya ce babu wanda ya rasa ransa a musibar da ta auku.
Ya ce yana wajen aiki lokacin da aka kira aka sanar da shi abin da ya faru, wanda kafin isarsa makwabtansa sun taimaka wajen janye motocinsa daga gidan.
Daraktan Hukumar Kwana-kwana na Jihar Ogun, ya ce da alama wutar ta samo tushe ne daga dakin girke-girke na gidan.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
