Connect with us

Sports

Ana Binciken Dani Alves Kan Cin Zarafin Wata Mata A Gidan Rawa

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA

 

 

Wata kotu a Sifaniya na binciken tsohon dan wasan bayan tawagar kwallon kafa ta Brazil Dani Alves kan zargin cin zarafin wata mata a gidan rawa.

 

Kotun da ke Barcelona ta fara binciken ne a watan da ya gabata, bayan matar ta shigar da karar, tana mai zargin cewa ya sanya hannunsa a wani bangare na jikinta wanda bai kamata ba kuma ba tare da yardarta ba.

Advertisement

’Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 4 A Zamfara

 

Duk da sanarwar ba ta fito karara ta ambaci sunan Alves ba, majiyoyi da dama sun tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na AFP cewa a kansa za a yi binciken.

 

’Yan sandan birnin Catalan sun ce matar ta shigar da karar ce a ranar 2 ga watan Janairu, sai dai Alves ya musanta zargin.

 

Duk da kuma Alves ya amince cewa ya halarci gidan rawar a ranar har ya cashe, sai dai ya ce bai taba ganin matar ba a rayuwarsa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending