Connect with us

News

Za Mu Hukunta Duk Wanda Ya Ki Karbar Tsoffin Kudi —Ganduje 

Published

on

 

 

Gwamnatin Jihar Kano, ta yi gargadin cewa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen kwace lasisin wasu manyan ‘yan kasuwa ko kuma daukar mataki kan duk wanda ya ki karbar tsofaffin takardun kudi.

 

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, wanda ya yi wannan gargadin a wata sanarwa da Kwamishinan Yada Labarai, Malam Muhammad Garba ya fitar, ya ce har yanzu tsoffin takardun Naira ana ci gaba da amfani da su.

Boko Haram Ta Hallaka Malaman Makaranta Sama Da 2000 A Shekara 8

Ya ce Kotun Koli ta yanke hukuncin wucin gadi na tsawaita wa’adin amfani da tsofaffin takardun kudin Naira har zuwa ranar da za ta yanke hukunci.

Advertisement

 

Gwamnan ya ce ba za su lamunci yadda wasu ‘yan kasuwa, manyan kantuna, bankuna, gidajen abinci, otal-otal, kasuwanni, gidajen mai, da wuraren ajiye motoci, da dai sauransu ke kin karbar tsofaffin takardun kudin ba.

 

Ganduje ya kara da cewa rashin amincewa da kudin na kara dagula al’amura, kuma hakan na kara jefa mutane cikin tsaka mai wuya.

 

Sanarwar ta kara da cewa, “Ayyukan kasuwanci da na tattalin arziki sun yi matukar tasiri wajen sauya fasalin kudin Naira, kuma abin takaici wasu sun daina karbar tsofaffin kudi, lamarin da ya kara jawo wa jama’a wahala yayin gudanar da hada-hadarsu.

Advertisement

 

Ya ce jama’a sun sha wahala, don haka gwamnatin jihar ba za ta nade hannunta ba ta bar wasu su kara ta’azzara lamarin ba.

 

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da gudanar da sana’o’insu tare da kai rahoton duk wanda ya ki karban tsofaffin takardun Naira zuwa wuraren da suka dace.

 

Idan dai za a iya tunawa, a ranar Lahadin da ta gabata ne gwamnatin jihar ta kulle babban kantin sayayya na ‘Well Care’ saboda kin karbar tsoffin takardun kudin Naira.

Advertisement

 

A hannu guda kuwa

 

Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya jadadda cewar ranar 10 ga watan Fabrairu ne wa’adin amfani tsofaffin takardun Naira ya cika.

 

Emefiele ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da jami’an diflomasiyya a Ma’aikatar Harkokin Waje da ke Abuja a ranar Talata.

Advertisement

 

Lamarin ya lafa sosai tun bayan lokacin da aka fara biyan kudi a kan kanta wanda hakan ya rage dogayen layuka a ATM.

 

“Don haka babu bukatar la’akari da wani sauyi daga wa’adin ranar 10 ga Fabrairu,” in ji shi.

 

Bayanin na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun rudani game da umarnin kotun kolin wanda ta tsawaita wa’adin zuwa ranar 15 ga watan Fabrairu, don yanke hukunci kan karar da ke gabanta.

Advertisement

 

‘Yan Najeriya sun shiga rudani yayin da bankunan kasuwanci suka daina karbar tsoffin takardun tun daga ranar Litinin.

 

Da yake karin haske, Emefiele ya ce, “Wasu daga cikin shugabanninmu suna siyan sabbin takardun kudi suna ajiyewa saboda wata manufa saboda haka ba zan iya yin karin haske kan hakan ba.”

 

Emefiele ya ce babban bankin ya san irin wahalhalun da ‘yan Najeriya ke sha sakamakon canjin kudin, amma ya ce tsarin zai iya kawar da kashi 4 cikin 100 na hauhawar farashin kayayyaki.

Advertisement

 

Ya kuma yi bayanin cewa kamata ya yi a ce adadin kudin da ke zagawa a hannun al’umma ya kai kusan Naira biliyan 700.

 

In anjima ne dai ake sa rai Kotun Ƙolin zata yanke hukuncin kamar yadda ta ayyana a zaman farko da ta yi a makon da ya gabata.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending