Connect with us

News

An umarci sanatoci biyu mata su fice daga majalisa kan ‘tufafin da suka saka’

Published

on

 

Majalisar dattawan Kenya ta umarci sanatoci mata guda biyu da su fice daga zauren majalisar, saboda tufafin da suka sanya a lokacin da suka halarci zaman majalisar.

Advertisement

 

Ɗaya daga cikinsu ta saka riga marar hannu, ɗayar kuma saboda ganin ɗigon jini a wandonta kasancewar tana al’ada.

Advertisement

Boko Haram Ta Hallaka Malaman Makaranta Sama Da 2000 A Shekara 8

Sanata Gloria Orwoba ta shaida wa shugaban majalisar cewa lamarin jinin al’ada abu ne da ke aukuwa ga mata ba tare da sun shirya masa ba.

 

Advertisement

To amma an umarce ta da ficewa daga majalisar kasancewar ba a amince da ganin ɗingon jini a tufafi ba, dan haka dole ta sauya tufafi.

 

Advertisement

An kuma umarci takwararta Sanata Karen Nyamu da ta fice daga zauren majalisar sakamakon sanya riga marar hannu.

 

Advertisement

Sanatocin ɓangaren adawa sun yi ƙorafin cewa Ms Nyamu ta sanya tufafin da zai kawo rashin kunya a majalisar.

 

Advertisement

Shugaban Majalisar ya ce hakan saɓa wa dokar sanya tufafi ce ta majalisar, wadda ta tanadi cewa dole mata su sanya tufafin da za su kare mutuncinsu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending