News
Majalisa: Kudirin haramtawa likitocin Najeriya aiki a waje
Wani kudirin doka da zai hana likitocin Najeriya ficewa daga kasar har sai sun yi aikin tsawon shekaru 5 a cikin gida, ya tsallake karatu na biyu a majalisar wakilai.
Manufar dokar itace dakile karuwar adadin likitocin dake ficewa aiki waje, bisa kwadaituwa da kyakkyawan yanayi.
Mamba a majalisar, Ganiyu Abiodun Johnson ne ya dauki nauyin kudirin, wanda aka yi wa take da ‘kudirin yiwa dokar likitoci ta 2004 kwaskwarima’.
NAHCO ta fitar da kudin aikin Hajjin bana ga jahohin yankin Arewa.
Johnson yace zai fi kyautuwa likitocin su fara amfanar da cikin gida da kwarewar da suka samu karkashin kulawar kasa, akalla da shekaru 5 kafin su fice.
Zaman majalisar na ranar Alhamis, 6 ga watan Aprilu, karkashin jagorancin Femi Gbajabiamila ya amince da wannan kudiri a karatu na biyu.
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News1 day ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
