A ƙarshen mako ake sa ran komawa teburin sulhu domin ci gaba da tattaunawa tsakanin ɓagarori biyun da ke faɗa da juna a ƙasar Sudan.
Duk da yarjejeniyar kare fararen hula da barin kayan agaji kai wa garesu, an ci gaba da faɗa a wasu sassan birnin Khartoum.
Inda Jiragen sama ke ta ruwan harsasai ta sama, sannan sojoji na ta ɓarin wuta a wasu titunan birnin.
Bangaren lafiyar ƙasar ya samu koma baya, yayin da asibitoci da sauran cibiyoyin lafiya suka daina aiki.
Farashin magunguna ya yi tashin gwauron zabo, sakamakon ƙarancinsa, yayin da mutane ke cikin mayuwacin hali.
An zargi duka ɓangarori biyun da ke yaƙi da juna da take haƙƙin bil-adama a lokacin yaƙin.
