News
Kamfanin suka gina Shaguna da Otel a filin Daula Hotel sunyi barazanar gurfanar da Gwamnatin Kano a gaban Shari’a
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Kamfanin Lamash Properties Limited da suka gina Shaguna da Otel a filin Daula Hotel sunyi barazanar gurfanar da Gwamnatin Kano a gaban Shari’a bayanda Gwamnati mai ci ta rushe ginin a karshen mako.
‘Daya daga cikin Jami’an Kamfanin Alhaji Aliyu Abubakar cikin wata Sanarwa daya rabawa manema Labarai yace zasu nemi diyyar Naira Biliyan 10 bayan rushe musu Gini ba tare da anji ba’asi daga garesu ba.
Ya Kuma ce ba siyan wajen sukai ba, sun kulla yarjejeniyar aiki ta hadin Gwiwa wato PPP da Gwamnatin Kano cikin shekarar 2020 dan sake Gina Otel din me hade da Shaguna da rukunin gidaje. Wanda Kuma an Kula yarjejeniyar cewar kamfanin zai mallakawa Gwamnatin Kano rukunin Otel da suka sake ginawa Kuma tuni sunyi Hakan cikin watan Mayun daya Gabatar.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
